in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin sama na Nijeriya sun lalata sansanin jigilar kayayyaki na kungiyar Boko Haram
2016-04-14 10:50:36 cri
Sojojin sama na kasar Nijeriya sun lalata sansanin jigilar kayayyaki dake birnin Kangarawa dake jihar Borno a yankin arewa maso gabashin Nijeriya. Kakakin sojojin NAF Ayodele Famuyiwa ya fadi hakan ne a ranar Laraba wato 13 ga wata.

Ya ce, dalilin da ya sa aka dauki wannan mataki domin yin amfani da karfin sojojin saman Nijeriya wajen kawar da 'yan kungiyar Boko Haram a jihar.

Bayan da sojojin sama sun jefa boma-bomai, an samu fashewar abubuwa a wurin, abun da ya shaida cewa, kila akwai makamai da harsashi a wurin. Kakakin ya kara da cewa, ci gaba da daukar wannan mataki, lamari ne da zai iya taimakawa wajen kawar da Boko Haram daga wurin.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China