A cewar kakakin hukumar wasannin jihar Titi Oshodi-Eko, an shirya gudanar da gasar ne domin kara bunkasa harkokin wasanni, tare da karfafa kwarewar 'yan wasan jihar, wadanda ka iya wakiltar jihar a gasannin kasa da kasa.
Har wa yau wata sanarwa da hukumar ta fitar ta hakaito shugaban ta Adebamke Oloko na cewa, za a kara cikin nau'oin wasannin motsa jiki 24, kuma 'yan wasa daga jihohin kasar 6 ne ake sa ran za su hallara domin gwada basirar su.
Jahohin a cewar sanarwar sun hada da Lagos, da Oyo, da Delta, da Ekiti, da Ogun da kuma Ondo. Za kuma su aike da 'yan wasa 144 cikin ajujuwan gasar 3, wato ajin kwararru, da na matsakaita, da kuma na kanana. A karshen gasar dai za a baiwa mahalartan ta takardun shaidar shiga, da lambobin karramawa.(Saminu Alhassan)