in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministocin harkokin wajen Sin da Japan sun gana da juna game da raya huldar zumunta
2016-04-30 17:29:25 cri

Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya gana da sakataren harkokin waje na kasar Japan Kisida Fumio wanda ke yin ziyarar aiki a kasar Sin a yau Asabar a masaukin baki na Diaoyutai dake nan birnin Beijing.

Mista Wang ya bayyana cewa, kasashen Sin da Japan suna makwabta da juna, kuma kasar Sin tana fatan raya huldar sada zumunta tare da kasar Japan.

A sa'i daya kuma, Mr. Wang Yi ya bayyana bukatar raya wannan hulda bisa tushen girmama tarihi da cika alkawarran juna da kuma yin hadin gwiwa a maimakon nuna adawa ga juna. Yace Sin tana fata ziyarar Kisida za ta taka rawa mai yakini ga kyautata huldar dake tsakanin kasashen biyu.(Lami)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China