in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumar zaben Ghana tana garambawul don yin zabe mai inganci a watan Nuwamba
2016-04-09 13:02:25 cri
Hukumar zaben kasar Ghana ta ce ta fara yin gyare gyare don tabbatar da zabe mai inganci a kasar.

Shugabar hukumar zaben kasar Charlotte Osei ita ce ta tabbatar da hakan bayan wani bore da ya barke a ranar Alhamis data gabata a Kumasi, birni na biyu mafi girma a kasar wanda ke da tazarar kilomita 270 a arewacin babban birnin kasar.

Wasu kafafen yada labarum kasar sun rawaito cewar, gungun magoya bayan jam'iyyun adawa ne suka shirya zanga zangar, inka suka nemi a samar da ingantaccen katin zabe ga masu kada kuri'u a babban zaben kasar wanda za'a gudanar cikin wannan shekara.

Shugabar hukumar zaben ta ce, tuni hukumar da dukufa wajen aiwatar da wasu sauye sauye, wanda kotun kolin kasar ta amince da su, don samun zabe mai inganci da za'a gudanar a ranar 7 ga watan Nuwanba, sabanin 7 ga watan Disamba kamar yadda aka ambata lokutan baya.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China