Wata sanarwa da mahukuntan kasar suka futar a jiya Laraba, ta bayyana cewa, majalisar tsaron kasar ta yi bitar hare-haren baya-bayan da suka auku a wadannan kasashe da kuma harkokin leken asiri da ake gudanar game da ayyukan ta'addanci a yammacin Afirka.
Bugu da kari, majalisar tsaron kasar ta Ghana ta sake bitar shirin kota-kwana game da yaki da ta'addanci na kasar, ayyukan dakarun hadin gwiwa da sauran matakai da nufin tabbatar da tsaro a kasar.
Don haka, majalisar tsaron kasar ta shawarci jama'a da su rika sanya ido tare da yin taka tsan-tsan, sannan su rika kai rahoton duk wasu abubuwan da ba su amince da su ba ga hukumomin tsaro.
A ranar Talata ce shugaba John Dramani Mahama na Ghana ya jagoranci taron majalisar tsaron kasar da nufin bibiyar yanayin harkokin tsaron kasar.(Ibrahim)