in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An gudanar da gagarumin makoki a kasar Burkina Faso
2016-01-26 20:16:31 cri
Dubban jama'ar kasar Burkina Faso ne suka yi cincirindo a wuraren da aka kaddamar da hare-haren ta'addanci na ranar 15 ga watan nan, domin nuna alhinin rasuwar mutane 32, wadanda harin ya ritsa da rayukan su, baya ga wasu 71 da suka ji raunuka. An dai gudanar da taron nuna juyayin ne a Litinin din nan karkashin tsauraran matakan tsaro daga jami'an rundunar 'yan sandan kasar.

Da yake gabatar da jawabi ga mahalarta gangamin, shugaban kasar Burkina Fason Christian Kabore, ya ce shi da gwamnatin sa, da daukacin 'yan kasar na mika sakon ta'aziyyar rasa rayuka, ga iyalai da 'yan uwan mamatan. Ya ce maharan ba su da wani buri, wanda ya wuce jefa tsoro da firgici a zukatan al'ummar kasar, tare da fatan ganin sun dakile irin ci gaban da kasar ke samu.

Idan dai za a iya tunawa, a ranar Juma'a 15 ga watan nan ne wasu mahara dauke da makamai suka aukawa wani Otel, da wani wurin shan Kofi dake birnin Ouagadouou, fadar mulkin kasar ta Burkina Faso, lamarin da ya sabbaba mutuwa da jikkatar mutane da dama, ciki hadda baki 'yan kasashen waje.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China