in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Burkina Faso: An sako 'yar kasar Australiya Jocelyn Elliot da kungiyar AQMI ta sace a tsakiyar watan Janairu
2016-02-08 12:30:32 cri
Jocelyn Elliot, matar likitan nan dan kasar Australiya Ken Elliot, da su biyun kungiyar kishin islama Al-Qaida a reshen Magreb ( AQMI) ta sace a ranar 15 ga watan Janairu a arewacin kasar Burkina Faso, an sake ta a ranar Asabar da yamma, jim kadan bayan amsa alhakin wannan awon gaba, a cewar wata majiyar tsaro. Wannan majiya ta tabbatar da cewa tsofuwar wanda aka yi garkuwan da ita din ina zaton cewa tana karkashin kulawar hukumomin Nijar.

A cikin wani sakon rediyo, a ranar Asabar, kungiyar Al-Mourabitoune, dake tare da kungiyar AQMI a yankin Magreb, ta yi shelar sace wadannan ma'auratan biyu 'yan kasar Australiya, a ranar 15 ga watan Janairun da ya gabata a yankin arewacin Burkina Faso, a ranar da kuma da aka kai harin Ouagadougou, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutane kusan talatin. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China