in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Taoudera ya kama aiki a matsayin sabon shugaban kasar Afrika ta Tsakiya
2016-03-31 11:44:09 cri
Faustin Touadera ya yi rantsuwar kama aiki a matsayin sabon shugaban kasar Afrika ta Tsakiya a ranar Laraba. An mai da zaben nasa a matsayin wata alama ta kawo karshen tashin hankali na tsawon lokaci a kasar, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutane da dama da mutanen da suka rasa gidajensu.

A yayin bikin rantsar da shi, mista Touadera ya ce kasar Afrika ta Tsakiya za ta bude wani sabon babi bayan rikici.

Sabon shugaban kasar ya alkawarta gina wata kasa mai zaman lafiya, cikin hadin kai da cigaba. Domin cimma wannan buri ne kasar za ta kara karfafa tsaro da kwanciyar hankali. A bangaren tattalin arziki, mista Touadera ya bayyana zai aiwatar da sauye sauye kan harkokin kudi, kuma za'a karfafa cigaban kanana da matsakaitan masana'antu. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China