in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
G20 za ta sa kaimi ga kafa tsarin zuba jari da yin cinikayya
2016-03-25 11:13:51 cri
Ministan harkokin cinikayya na kasar Sin Gao Hucheng ya bayyana a jiya Alhamis 24 ga wata cewa, tare da canjin tattalin arzikin duniya, abin da kungiyar G20 ta maida hankali a yanzu shi ne sauyawa daga tinkarar rikicin hada-hadar kudi, zuwa sa kaimi ga bunkasuwar tattalin arziki. Mr. Gao ya ce a bana, kungiyar G20 za ta sa kaimi ga bangarori daban daban wajen inganta tsarin zuba jari da yin cinikayya.

Gao Hucheng ya bayyana a gun taro mai taken "lokacin yin kwaskwarima ga G20: cimma burin duniya ta hanyar shirin kasar Sin" na dandalin tattaunawa na Asiya na Bo'ao na shekarar 2016 da aka gudanar a jiya Alhamis, cewa yanzu ana samun raguwar ciniki a duniya, kuma ana bukatar matakin inganta zuba jari a tsakanin kasa da kasa. Don haka kungiyar G20 ke da alhakin daukar matakai don taka muhimmiyar rawa, wajen sa kaimi ga bunkasar harkar zuba jari da cinikayya a duniya.

Haka zalika kuma, Gao Hucheng ya ce, Sin tana fatan kokari tare da bangarori daban daban, don sa kaimi ga kungiyar G20, ta yadda za ta samu kyakkyawan sakamako a fannin tattalin arziki, da cinikayya, don amfanar dukkanin duniya a tsawon lokaci. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China