in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU ta yi Allah wadai da harin Brussels
2016-03-23 11:02:25 cri
Kungiyar tarayyar Afrika AU ta yi Allah wadai da harin ta'addacin da aka kaddamar a birnin Brussels na kasar Belgium wanda ya yi sanadiyyar hallaka rayukan mutane a kalla 34 da jikkata wasu sama da 200.

A wata sanarwar da Nkosazana Dlamini-Zuma, shugabar AU ta fitar da a yammacin ranar Talata, ta yi Allah wadai da harin wanda aka kaddamar a filin jirgin sama na Zaventem da kuma babbar tashar jirgin kasa na Brussels, harin wanda ya yi sanadiyyar kashe fararen hula wadanda ba su ji ba su gani ba, da kuma raunata mutane masu yawa.

Dlamini-Zuma ta gabatar da sakon ta'aziyyar AU ga gwamnati da al'ummar kasar Belgium, da iyalan wadanda harin ya rutsa da su, tare da yin fatan samun lafiya ga wadanda suka samu raunuka a yayin harin.

Sannan ta jaddada aniyar AU ta kyamar dukkan nau'in ta'addanci da tsattsauran ra'ayi. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China