in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumomin shiga tsakani a rikicin Syria sun isa kasar don shirin tsagaita wuta
2016-02-12 12:50:09 cri
Manyan jami'an hukumomin kasa da kasa masu shiga tsakani kan rikicin Syria sun amince da aiwatar da dukkanin matakan da za su tabbtar da tsagaita wuta a kasar wacce ke fama da rikici a yankin gabas ta tsakiya.

Bayan tattaunawa ta tsawon lokaci wanda kasashen Amurka da Rasha suka jagoranta, kungiyoyin kasa da kasa dake fafutukar tabbatar da zaman lafiya a Syria, sun amince da'a shigar da kayayyakin tallafi zuwa kasar.

Da yake jawabi ga manema labaru a yau Jumma'a, sakataren harkokin wajen Amurka John Kerry ya ce, shirin tsagaita wutar a fadin kasar na tsawon mako guda, zai ba da damar shigar da kayayyakin jin kai ga dinbin fafaren hula dake cikin mawuyacin halin a kasar.

Ya kara da cewar, kawo yanzu ba'a bayyana yadda shirin tsagaita wutar zai gudana ba.

Sai dai mahalarta taron tattauna kan batun tsagaita wutar sun bukaci da a maido da batun tattaunawar zaman lafiya ta Geneva. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China