in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU ta yi Allah wadai da harin da aka kai Burkina Faso
2016-01-18 11:13:15 cri
Kungiyar hadin kan nahiyar Afirka ta AU, ta bayyana matukar takaici game da harin ta'addanci da aka kaddamar a kasar Burkina Faso a ranar Juma'a, harin da ya hallaka mutane 29 tare da jikkata wasu mutum 30.

Da take bayyana alhinin ta game da aukuwar harin, shugabar kwamitin zartaswar kungiyar ta AU uwargida Nkosazana Dlamini Zuma, ta ce AU za ta ci gaba da baiwa Burkina Faso da al'ummar ta goyon bayan da ya dace. Ta ce kwamitin tana matukar Allah wadai da aukuwar wannan lamari na rashin imani, wadda ya salwantar da rayukan fararen hula da ma wasu jami'an tsaro.

Zuma ta kuma gabatar da sakon ta'aziyya ga iyalan wadanda suka rasu, tare da fatan samun sauki ga wadanda suka jikkata. Ta ce harin na baya bayan nan na zuwa a daidai gabar da sabuwar gwamnatin kasar ta maye gurbin gwamnatin rikon kwarya, a wani mataki na wanzar da tsarin dimokaradiyya, da adalci, tare da hada kan 'yan kasar, da kuma tabbatar da ci gaban kasar da ma yankin baki daya.

Uwargida Zuma ta kuma bayyana muhimmancin hadin gwiwar kasa da kasa da na shiyya shiyya, game da yakin da ake yi da ayyukan ta'addanci a daukacin sassan nahiyar Afirka. Ta ce ya zama wajibi sassan masu ruwa da tsaki su hada karfi da karfe wajen cimma nasarar wannan yaki. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China