160107-Kocin-kungiyar-wasan-kwallon-kafa-ta-Najeriya-yace-sun-shirya-tsab-don-shigar-gasar-cin-kofin-kasashen-Afrika-zainab.m4a
|
A wata hira ta wayar hannu da kamfanin dillancin labaran kasar Sin Xinhua, kocin na Najeriya ya ce, 'yan wasan na Super Eagles na zaune cikin shirin ko ta kwana, za kuma su taka rawar gani a gasar da za a bude ranar 16 ga wannan wata na Janairu.
Ya kara da cewar, tuni aka killace 'yan wasan a birnin Pretoria na kasar Afrika ta kudu domin basu horo na musamman, ta yadda zasu iya tunkarar duk wani kalubale daga abokan karawar su, su kuma dauko kofin zuwa gida Najeriya.
Ana saran tawagar 'yan kwallon ta Najeriya zata zarce kasar ta Rwanda bayan kammala samun horon a Afrika ta kudu.(Ahmad Fagam)