in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Fasahar bunkasa aikin noma ta Sin na samun karbuwa a Guinea-Bissau
2016-01-06 11:16:00 cri

Tawagar kungiyar manoman Guinea-Bissau (ANAG) za ta kawo ziyarar kasar Sin domin kammala sanya hannu kan yarjejeniyoyin hadin gwiwa tare da takwarorinsu na kasar Sin, in ji shugaban kungiyar James Gomes a ranar Talata.

Mista Gomes ya bayyana cewa wannan yarjejeniyar ta kunshi wani tallafin kasar Sin wajen horar da kuma samar da kayayyakin aiki gona ga kungiyar ANAG.

A shekarar 2015, manoma da kwararru Guinea-Bissau fiye da 60 suka samu horo a nan kasar Sin, domin samun damar kara kyautata bunkasa noma a kasar Guinea-Bissau, in ji mista Gomes.

Kungiyar ANAG na fatan samun na'urorin noma domin bunkasa noma a Guinea-Bissau, inda har yanzu kusan kashi 90 cikin 100 na manoman kasar suke aikin noma a gargajiyance. Gomes ya kara da cewa, suna iya kara bunkasa samar da albarkatun noma bisa hulda da kasar Sin, sakamakon kasancewar kasarsa a matsayin wata kasa ta noma. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China