in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin tsaro na MDD ya bukaci bangarorin gwamnatin kasar Guinean Bissau da su hau teburin sulhu.
2015-08-13 10:43:13 cri
Kwamitin tsaro na MDD ya bukaci shugabannin siyasar kasar Guinea Bissau da su hau teburin sulhu domin yin aiki tare da samar da gwamnatin hadin kai kasancewar gwamnatin kasar ta kafu ne a dai dai lokacin da kasar ke fuskantar rikicin shugabanci a kwanakin baya.

A sanarwar da kwamitin mai mambobi 15 ya fitar ya ce ya lura da irin takun sakar dake wanzuwa tsakanin bangaren shugaban kasa da na firaministan kasar wanda hakan na iya mayar da hannun agogo baya ga cigaban kasar tun bayan dawowar tsarin gwamnati mai bin doka da oda bayan kammala babban zaben kasar a shekarar 2014.

Rahotannin sun bayyana cewar rashin jituwar dake wanzuwa tsakanin bangaren shugaban kasar da firaiministan zai iya jefa kasar cikin tashin hankali.

Kwamitin MDD ya jaddada bukatar bangarorin biyu da su dinke barakar dake tsakaninsu ta hanyar hawa teburin sulhu da gudanar da gwamnati mai tsabta da shimfida tsarin mulki na fararen hula mai cike da 'yanci, ta haka ne kadai kasar za ta samu dawamamman zaman lafiya.

Kazalika kwamitin na MDD ya bayyana muntunta dokokin kasa da kula da hakkin al'ummar kasar na daga cikin abubuwan da za su taimakawa kasar ta Guinea Bissau samun zaman lafiya mai dorewa. (Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China