in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 39 sun mutu a gumurzu tsakanin sojojin DRC da 'yan tawayen ADF na Uganda
2015-12-10 11:14:03 cri
Gumurzu na ranar 29 ga watan Nuwamba tsakanin rundunar sojojin DRC-Congo na FARDC da 'yan tawayen Uganda na ADF ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 39 a yankin Beni dake cikin gundumar Arewacin Kiwu, in ji laftanal kanal Amouzoun Codjo Martin, kakakin sojojin tawagar wanzar da zaman lafiya ta MDD dake Congo MONUSCO.

A ranar 2 ga watan Disamban shekarar 2015, adadin wadannan hare hare ya nuna cewa, an kashe sojin MDD guda, da sojojin FARDC bakwai, fararen hula goma da kuma 'dan tawayen ADF guda, in ji mista Amouzoun Codjo Martin, a ranar Laraba a yayin wani taron manema labarai na MDD.

A cewarsa, sojojin MONUSCO suna ci gaba da ayyukan soja a gundumar Arewacin Kivu, tare da hadin gwiwar sojojin FARDC, domin kawar da mayakan ADF. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China