in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rwanda za ta shirya raba gardama kan kundin tsarin mulki a ranar 17 ga Disamba
2015-12-10 11:12:52 cri
Kasar Rwanda na shirin gudanar da raba gardama kan yi wa kundin tsarin mulki gyaren fuska domin baiwa shugaban kasa Paul Kagame yin tazarce bayan shekarar 2017 a ranar 17 ga watan Disamba, in ji wata sanarwa ta fadar shugaban kasa.

Sanarwar da aka fitar bayan wani taron ministoci na gaggawa da shugaba Kagame ya jagoranta, ta nuna cewa, 'yan kasar Rwanda dake kasashen waje za su jefa kuri'a a ranar 17 ga watan Disamban shekarar 2015 a yayin da wadanda suke cikin kasa za su jefa a ranar 18 ga watan Disamba. Bisa tanade tanaden kundin tsarin mulki da sauran dokoki, shugaban jamhuriya ya ba da amincewarsa wajen shirya wani zaben raba gardama kan kundin tsarin mulkin da aka yi wa gyaren fuska a shekarar 2015 bisa ga na ranar 4 ga watan Yunin shekarar 2003, in ji wannan sanarwa. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China