in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
CAD da hukumomin kasa da kasa sun hada kai don sa kaimi ga hadin gwiwa a nahiyar Afirka
2015-12-04 11:19:26 cri

A jiya ne aka bude taron 'yan kasuwa na kasashen Sin da Afirka karo na 5 a birnin Johannesburg dake kasar Afirka ta Kudu, inda asusun raya Sin da Afirka wato CAD ya daddale yarjejeniyoyin hadin gwiwa tare da hukumar raya masana'antu ta MDD wato UNIDO, asusun Melinda Gates, asusun Africa 50 da kuma kungiyar 'yan kasuwa ta kasa da kasa ta kasar Sin.

A jawabinsa yayin taron shugaban asusun CAD Chi Jianxin ya bayyana cewa, asusun CAD ya hada kai tare da hukumomin kasa da kasa ta yadda za a zuba jari a Afirka, tare da karfafa hadin gwiwa a Afirka, fadada yankunan zuba jari, da janyo karin kamfanonin Sin su kara zuba jari a nahiyar Afirka ta yadda za a gaggauta raya tattalin arziki da inganta rayuwar al'ummomin kasashen Afirka. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China