in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumar DSS a Najeriya ta kama shugaban AIT
2015-12-02 09:35:30 cri
Hukumar tsaron fari kaya a Najeriya wato DSS a takaice ta kama shugaban gidan talabijin mai zaman kansa na AIT Raymond Dokpesi dangane da binciken da ake gudanarwa kan badakalar sayen makamai da ake zargin ofishin mai baiwa tsohon shugaban Najeriya ta fuskar tsaro kanar Sambo Dasuki da aikatawa. Ana zargin Dokpesi ne da karbar Naira biliyan 2.1 daga ofishin na NSA.

Kama shugaban gidan talabijin na AIT dai na zuwa ne a bayan kame Sambo Dasukin da hukumar ta DSS din ta yi domin ya amsa tambayoyi game da dala biliyan biyun da aka ce an yi amfani da su wajen sayen makaman.

A wani labarin kuma, hukumar EFCC ta damke tsohon gwamnan jihar Sokoto da ke arewa maso yammacin Najeriya Attahiru Bafarawa dangane da wancan badakalar sayen makaman.

Bugu da kari, hukumar ta EFCC tana farautar tsohon shugaban jam'iyyar PDP Mohammed Haliiru Bello da shi ma ake zargi da karkatar da wasu kudaden sayen makaman.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China