in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ya kamata Rasha da Turkey su kara tuntubar juna, in ji kakakin Sin
2015-11-27 20:37:41 cri
Yaki da ta'addanci, wani nauyi ne da aka dora kan wuyan kasashen duniya baki daya. Kamata ya yi kasashen Rasha da Turkey su kara tuntubar juna, a kokarin hana lamarin kara yin kamari, in ji Hong Lei, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin.

Hong Lei ya fadi haka ne a yau Jumma'a 27 ga wata yayin taron manema labaru da aka saba shiryawa a nan Beijing, inda aka tabo batun cewa, shugaba Vladimir Putin na Rasha ya ce, kasarsa na jiran Turkey ta nemi gafara ko ta biya diyya sakamakon harbo jirgin saman sojan Rasha.

Sannan kuma kakakin kasar na Rasha ya bukaci Turkiya da ta yi bayani kan lamarin. A waje daya kuma, Turkiya ta ce, ta harbo jirgin Rasha ne bisa umurni, don haka babu bukatar neman gafara daga wajen Rasha.

Hong Lei ya kara da cewa, an harbo wani jirgin saman sojan Rasha, har ma ya sa wani matukin jirgin ya rasu, lamari ne maras sa'a, kasar Sin ta tausaya lamarin. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China