in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban majaliwar ba da shawara kan harkokin siyasan kasar Sin ya gana da shugaban majalisar dattawan kasar Zimbabwe
2015-09-18 21:48:21 cri
A yau Juma'a ne, shugaban majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa na kasar Sin Yu Zhengsheng ya gana da shugaban majalisar dattawan kasar Zimbabwe Edna Madzongwe a nan birnin Beijing.

A yayin ganawar, Yu ya ce, dangantakar dake tsakanin Sin da Zimbabwe abin koyi ne wajen hadin kai tsakanin Sin da kasashen Afirka. Ya kara da cewa, Sin na mayar da hankali sosai kan dangantakar abokantaka dake tsakanin kasashen biyu, tana kuma fatan bangarorin biyu za su yi kokarin tabbatar da ra'ayoyin da shugabanninsu suka cimma.

A nasa bangaren Madzongwe ya bayyana cewa, majalisar dattawan kasar Zimbabwe na son karfafa hadin kai da cudanya tare da majalisar ba da shawara kan harkokin siyasan kasar Sin, don ciyar da dangantakar dake tsakanin kasashen biyu gaba. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China