in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba Xi Jinping ya nemi a yi rigakafi da dakile matsalolin annoba kamar yadda ya kamata
2015-11-25 19:16:15 cri
A yau ne a nan birnin Beijing, gwamnatin kasar Sin ta shirya wani babban taron yabawa nasarorin da aka samu wajen rigakafi da dakile matsalar annobar cutar Ebola, inda a sakon da ya aiko a taron, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya ba da wani muhimmin umurni game da aikin rigakafi da yadda za a dakile matsalolin annoba.

Xi Jinping ya nuna cewa, bayan da annobar cutar Ebola ta barke a wasu kasashen yammacin Afirka, nan da nan kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin da majalisar gudanarwa ta kasar sun tsai da kudurin tallafawa kasashen Afirka wadanda suke fama da cutar bisa namijin kokarinta na kara sada zumunta tsakanin kasashen Sin da Afirka. Wannan ya alamta cewa, kasar Sin babbar kasa ce dake kokarin sauke nauyin da ke kanta, kuma ta bayar da muhimmiyar gudummawarta wajen karfafa da kuma bunkasa zumuncin dake kasancewa tsakanin kasashen Sin da Afirka.

Bugu da kari, shugaba Xi Jinping yana fatan hukumomin gwamnatoci na matakai daban daban da na soja za su ba da muhimmanci ga batun tabbatar da lafiyar jama'a, kana su dauki kwararan matakai na yin rigakafi da shawo kan duk wata annoba cikin lokaci, ta yadda za a tabbatar da ganin cewa kasar Sin ta zama kasar da al'ummominta suke zaune cikin koshin lafiya, kuma za su iya bayar da gudummawarsu wajen cimma burin bunkasuwar kasar Sin baki daya. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China