in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
ECOWAS za ta tura tawagar sanya ido a zaben shugaban kasar Burkina Faso
2015-11-24 10:38:56 cri
Tsohon shugaban rikon kwarya na kasar Guinee-Bissau, Manuel Serifo Nhamadjo, zai jagoranci tawagar sanya ido kan zabe ta kungiyar raya tattalin arzikin yammacin Afrika (ECOWAS) a zaben shugaban kasar Burkina Faso da za'a shirya a ranar 29 ga watan Nuwamba mai zuwa, in ji wata sanarwar kungiyar a ranar Litinin a birnin Cotonou.

Wannan tawaga, da kungiyar shiyyar ta tura bisa tushen yarjejeniyar dake nuna fifiko kan tsarin demokaradiyya da shugabanci na gari, za a daura mata nauyi musamman ma wajen tabbatar ganin an gudanar da zabe cikin 'yanci da kwanciyar hankali da adalci. Kuma za ta kunshi masu sa ido 133, da za a tura zuwa yankunan kasar baki daya, domin su sanya ido kan yadda dukkannin ayyukan zabe za su gudana.

Bayan zaben, in ji wannan majiya, tawagar sa ido ta ECOWAS za ta iya bayyana ra'ayinta ko ma gabatar idan akwai bukata da wasu shawarwari zuwa ga dukkan masu ruwa da tsaki da zaben ya shafa. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China