in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
UNHCR ta ce mutane miliyan 2.2 ne rikicin Boko Haram ya raba da gidajen su a Najeriya
2015-11-20 10:15:48 cri
Hukumar kula da 'yan gudun hijira ta MDD wato UNHCR, ta ce a halin da ake ciki, yawan mutanen dake rayuwa a sansanin 'yan gudun hijira a shiyyar arewa maso gabashin Najeriya ya karu zuwa miliyan 2 da dubu 200.

Wakiliyar hukumar ta UNHCR a Najeriya, Angele Dikongue-Atangana, ta sanar da wannan kididdiga a ranar Alhamis din nan a Abuja babban birnin kasar, a yayin taron ganawa da masu ruwa da tsaki na hukumar na shekarar 2015.

Dikongue-Atangana, ta ce hukumar ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen tallafawa wadanda matsalar ta shafa, sannan ta bukaci sauran hukumomin bada tallafi na duniya da su tallafawa mutanen da matsalar ta shafa.

Ta kara da cewar, a wannan shekarar ta 2015, hukumar ta UNHCR ta samu nasarori masu yawa a Najeriyar, musamman wajen tsugunar da wadanda rikicin ya raba da matsugunan su, da kuma samar da hadin gwiwa da hukumar ECOWAS.

A cewarta, hukumar ta taimaka wajen mayar da wasu 'yan asalin jamhuriyar Kamaru su 452 zuwa gidajen su, sannan ta ce a halin yanzu, an shirya sake mayar da karin wasu mutanen kimanin 165 zuwa kasashensu wadanda ke gudun hijira a yankunan kasashen Turai da Amurka.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China