in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban hukumar wasan kwallon kafar Jamus ya amince da bada na goro ga hukumar FIFA gabanin karbar bakuncin gasar cin kofin duniya ta 2006
2015-11-05 16:18:47 cri
A kwanakin baya, mujallar Der Spiegel ta kasar Jamus ta bayar da wani labari dake cewa, hukumar wasan kwallon kafar kasar Jamus ta taba baiwa hukumar wasan kwallon kafa ta duniya wato FIFA cin hanci. Game da hakan, shugaban hukumar wasan kwallon kafar kasar Wolfgang Niersbach, ya gudanar da taron gaggawa na manema labaru, inda ya amince da baiwa hukumar ta FIFA wasu kudade kafin a yarda kasar sa ta karbi bakuncin gasar cin kofin duniya da ya gudana a shekarar 2006, dai ya tabbatar da cewa wannan kudi ba cin hanci ba ne. kuma ba kudin ne da aka yi amfani da shi don sayen kuri'un goyon baya ba.

Mujallar Der Spiegel ta bayar da labari cewa, kwamitin neman daukar bakuncin gasar cin kofin duniya na kasa Jamus na wancan lokaci ya taba baiwa hukumar FIFA cin hanci da yawansu ya kai kudin Swiss Franc miliyan 10.3 don tabbatar da samun kuri'un goyon baya daga wakilai hudu daga nahiyar Asiya.

Ya kara da cewa a shekara ta 2002, shugaban hukumar FIFA na lokacin Sepp Blatter, ya zanta da shugaban kwamitin neman daukar bakuncin gasar cin kofin duniya na kasar Jamus Franz Beckenbauer, inda Balatter ya yi alkawarin samar da kudi Swiss Franc miliyan 250 don taimakawa kasar Jamus, wajen daukar bakuncin gasar cin kofin na duniya, amma da farko sharadi shi ne hukumar wasan kwallon kafa ta Jamus ta biya kudi Euro miliyan 6.7 ga hukumar FIFA tukuna. A lokacin Beckenbauer ya nuna aniyar sa ta bayar da wadannan kudade, amma mashawarcinsa ya ki amincewa. A karshe dai, tsohon shugaban kamfanin Adidas ya biya kudin.

Amma Niersbach bai bayyana dalilin hukumar wasan kwallon kafar kasar Jamus ba game da biyan wannan kudi, kana ya ce ya san wannan batu a yayin tattaunawar sa da Beckenbauer a 'yan kwanakin baya.

A halin yanzu, hukumar FIFA da hukumar wasan kwallon kafa ta Jamus suna gudanar da bincike kan wannan batu.(Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China