Ministan harkokin waje na kasar Rasha Sergei Lavrov ya sake tuntubar sakataren harkokin waje na kasar Amurka John Kerry ta wayar tarho domin tattauna batun kasar Sham a jiya Litinin, ta haka ya zama kwanaki 3 a jere da ministocin harkokin wajen kasashen biyu suka dinga tuntubar juna ta wayar tarho game da rikicin Syria.
Ma'aikatar harkokin waje ta kasar Rasha ta bayar da sanarwa a wannan rana cewa, bangarorin biyu sun tattauna sosai kan yadda za a gudanar da yunkurin siyasa domin warware rikicin kasar Sham.(Lami)