in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Amurka za ta daina ba da horo ga kungiyar adawa ta kasar Sham
2015-10-10 13:59:35 cri

Ma'aikatar tsaron Amurka ta furta a jiya Jumma'a cewar, sojojin kasar za su daina shirin su na horas da kungiyar adawa ta kasar Sham, a maimakon hakan, za su bada goyon bayansu ta wata hanya ta daban domin yaki da kungiyar IS.

Mataimakiyar ministan tsaron Amurka Christine Warmouth ce ta bayyana hakan yayin wani taro. Ta ce yanzu sojojin Amurka sun tsayar da shirin ba da horo ga kungiyar adawa ta kasar Sham sakamakon wasu kalubaloli masu tsanani da suke fuskanta.

Christine, ta kara da cewar, sojojin Amurkan za su samar da jiragen saman yaki da makamai ga dakarun adawa na kasar Sham don amfani da su wajen yaki da kungiyar IS.(Lami)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China