in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kafofin yada labarai na kasa da kasa suna mai da hankali sosai kan hadin gwiwa tsakanin Sin da Birtaniya
2015-10-22 18:51:31 cri
A jiya Laraba ne shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi shawarwari da firaministan kasar Birtaniya David William Donald Cameron, inda bangarorin biyu suka yanke shawarar kulla dangantakar abokantaka bisa manyan tsare tsare tsakanin kasashen biyu a sabon karni na 21, tare da halartar bikin rattaba hannu kan yarjeniyoyin hadin gwiwa a fannonin hada hadar kudi da kwastan da sauransu. Kafofin yada labarai na duniya suna ganin cewa, rattaba hannu kan yarjejeniyar cinikayya tsakanin Sin da Birtaniya zai kara bunkasa hadin gwiwa tsakaninsu zuwa wani sabon mataki.

A jiya kamfanin dillancin labaru na Reuters ya ba da labarin cewa, shugaba Xi ya tattauna da firaminista Cameron ofishinsa kan yarjejeniyar da darajarta ta kai sama da dala biliyan 10,inda daga bisani suka daddale yarjejeniyar samar da wutar lantarki bisa makamashin nukiliya. Wannan ne karo na farko da Sin ta zuba jari da yawa kan tashar makamashin nukiliya a kasashen yammacin duniya. Kasar Birtaniya tana kokarin kyautata kashi daya bisa hudu dangane da karfinta na samar da wutar lantarki cikin shekaru 10 masu zuwa. Jarin da Sin ta zuba zai kara ba ta wani sabon karfi da zarafi a fagen gwada fasaharta a fannin makamashin nukiliya.

Bayan haka, kamfanin dillancin labaru na AFP ya ba da labarin cewa, Birtaniya na fatan kara samun jari daga kasar Sin sakamakon ziyarar da shugaba Xi Jinping ya kawo.

A yau kuma, jaridar Lianhe Zaobao ta Singapore ta rubuta wani labari mai taken "Yanayin da duniya ke ciki a karkashin huldar diplomasiyyar da ke tsakanin Sin da Birtaniya", inda ta ce, Birtaniya tana kokarin zurfafa dangantaka tsakaninta da Sin. Sakataren kudin Burtaniya da aka saran cewa zai zama firaministan kasar a karo mai zuwa, ya sa kaimi ga gudanar da wannan batu. Yana ganin cewa, bunkasuwar Sin za ta kawo sabon zarafi ga kasar Birtaniya a fannin bunkasa tattalin arziki, a sabili da haka, ya kalubalanci shiga wani sabon zamani na shekaru 10 wajen kyautata dangantaka tsakanin Sin da Birtaniya.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China