in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Xi ya gana da takwaransa na kasar Chadi
2015-10-15 21:29:09 cri
Shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya bayyana cewa, kasar Sin sahihiyar kawa ce da za ta taimakawa kasar Chadi bunkasa masana'antunsu.

Shugaba Xi wanda ya bayyana hakan a yau, lokacin da yake ganawa da takwaransa na kasar Chadi Idriss Deby a nan birnin Beijing. Ya kuma ce yana maraba da shugaba Deby da ya halarci taron manyan jami'ai kan hanyoyin rage talauci da raya kasa da zai gudana a nan birnin Beijing.

Shugaba Xi ya ce, kasar Chadi muhimmiyar abokiyar hadin gwiwar kasar Sin ce, kuma kasar Sin na dora muhimmanci kan hadin gwiwar da ke tsakaninsu.

Bugu da kari, shugaba Xi ya bayyana cewa, kasar Sin a shirya ta ke ta hada kai da kasar Chadi wajen cimma nasarar zamanantar da bangaren masana'antun kasar.

Don haka, shugaba Xi yana kira ga sassan biyu da su kara karfafa amince da fahimtar junan da ke tsakaninsu kan manyan batutuwan kasa da kasa. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China