in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Burkina Faso: Yanzu doka za ta rika aiki ga masu laifukan cin zarafin mata
2015-09-08 10:48:44 cri
Majalisar dokokin wucin gadi ta Burkina Faso ta amince a ranar Lahadi da dokar ta shafi rigakafi, hukunta laifukan da suka shafi cin zarafin mata da kananan 'yan mata da kuma daukar nauyin wadanda matsalolin suka shafa.

A cewar 'yan majalisun, wannan wata dama ce ta cike gibin shari'a a wannan fanni. A cewar wannan sabuwar doka, duk mutanen da aka tabbatar da aikata wadannan laifuka na cin zarafin mata, za'a yanke musu hukuncin zaman yari har na zuwa shekaru biyar da cin su tara ta kusan Sefa jika dari shida zuwa miliyan 1,5 kimanin dalar Amurka dubu guda zuwa dubu biyu da dari biyar, ko kuma daya daga cikin wadannan hukunce hukunce biyu kawai. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China