in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-moon ya yi maraba da Burkina Faso da ta zartas da tsarin dokoki na wucin gadi
2014-11-15 10:44:54 cri
Magatakardar MDD Ban Ki-moon a jiya Juma'a ya bayar da wata sanarwa ta bakin kakakinsa, inda ya yi maraba ga bangarori daban daban na kasar Burkina Faso da su zartas da tsarin dokoki na wucin gadi, ya kuma kara musu kwarin gwiwa wajen ci gaba da tattaunawa a yunkurin kafa gwamnatin wucin gadi.

A cikin sanarwar, an ce bisa wannan tsarin dokoki na wucin gadi shugaban farar hula na kasar Burkina Faso zai iya gudanar da harkokin kasa na tsawon shekara guda yadda ya kamata. Ban Ki-moon yana fatan za a sa hannu kan tsarin dokokin, kuma shugaban farar hula na wucin gadi zai ci zabe da kuma yin rantsuwar kama aikinsa, kana hukumar wucin gadi za ta fara aiki yadda ya kamata.

Bayan haka kuma, sanarwar ta ce, Ban Ki-moon ya nuna yabo ga bangarori daban dabban na kasar ta Burkina Faso saboda kokarin da suka yi a yayin tattaunawar da aka gudana a duk fadin kasar, da kuma nauyin da suke dauka bisa wuyansu. Haka zalika Ban Ki-moon ya nuna yabo ga kokarin da MDD, da tawagar hadin kai ta AU da ECOWAS, da kuma kasashen duniya suka yi na shiga tsakani a rikicin kasar Burkina Faso. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China