in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugabannin Togo da Senegal na kokarin shiga tsakanin game da rikicin milka mulki a Burkina Faso
2014-11-12 16:22:54 cri
Shugaba Faure Gnassingbe na Togo da takwaransa na Senegal Macky Sall sun ziyarci kasar Burkina Faso a kokarin sasanta rikicin mika mulki da ake fama da shi a kasar, sakamakon kwace mulki da sojojin kasar suka yi bayan murabus din Blaise Compore daga karagar mulki.

Ziyarar shugabannin biyu ta zo ne yayin da jam'iyyun siyasar kasar da kungiyoyin fararen hula suka gabatarwa jagoran rikon kwaryar kasar Laftana kanar Isaac Zida wani daftari wanda ke kunshe da shirin mika mulki ga hannun farar hula,kafa gwamnatin rikon kwarya mai mambobi 25 da 'yan majalisun dokokin rikon kwarya guda 90.

Bugu da kari a ranar Litinin ma shugaban kasar Muaritania kana shugaban kungiyar tarayyar Afirka (AU) Mohamed Ould Abdel Aziz ya gana da dukkan bangarorin da abin ya shafa don ganin an taimakawa kasar ta Burkina Faso lalubo hanyoyin warware wannan matsala da kanta ta hanyar mika mulki ga hannun farar hula.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China