in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-moon zai halarci bikin faretin tunawa da cika shekaru 70 da kawo karshen harin Japanawa
2015-08-25 13:44:53 cri
Babban satakaren MDD Ban Ki-moon zai halarci bikin faretin tunawa da cika shekaru 70 da kawo karshen harin Japanawa da kasar Sin za ta shirya a ranar 3 ga watan Satumba.

Mataimakin babban sakataren MDD Jan Eliasson ne ya bayyana hakan jiya Litinin a cibiyar MDD dake birnin New York yayin da yake halartar bikin nune-nunen hotuna game da tunawa da cika shekaru 70 da kawo karshen harin Japanawa, da yaki da ra'ayin masu nuna karfi a duniya da kuma kafuwar MDD.

Da ya ke tsokaci game da bikin faretin da kasar Sin za ta shirya, Eliasson ya bayyana cewa, babban sakataren MDD Ban Ki-moon zai halarci bikin saboda muhimmancin ranar 3 ga watan Satumba. Ban yana fatan wannan biki ya kasance wata dama ta koyi da abubuwan da suka faru a tarihi, da kuma yin imani da shimfida zaman lafiya bisa tushen tsarin mulkin MDD a nan gaba.

Hakazalika kuma, Eliasson ya ce, Sin muhimmiyar kawar MDD ce, yana fatan kasar Sin da MDD za su ci gaba da yin hadin gwiwar a nan gaba. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China