in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba Xi ya bukaci a aiwatar da gyare-gyare kamar yadda aka tsara
2015-08-18 20:55:33 cri
Shugaban Xi Jinping na kasar Sin ya bukaci JKS da kuma jami'an gwamnatin kasar da su himmatu wajen ganin an aiwatar da gyare-gyaren da aka tsara ta yadda kwalliya za ta biya kudin sabulu.

Shugaba Xi ya yi wadannan kalamai ne yayin taron babban kwamitin kula da yin gyare-gyare na kasa karo na 15.

Tun lokacin da aka fara zurfafa yin gyare-gyare a sassa daban-daban na kasar, aka fara ganin kyakkyawan sakamako a farkon wannan shekara.

Don haka ya jaddada cewa, wajibi ne bangaren JKS da gwamnati a dukkan matakai su kara zage damtse da nuna juriya wajen kara zurfafa yin gyare-gyare, tare da fito da matakan magance sabbin matsalolin da suka kunno kai yayin da ake aiwatar da wadannan gyare-gyare.

A karshen shekarar 2013 ne aka kafa wannan kwamiti domin sa-ido kan yadda shirin zurfafa yin gyare-gyaren ke gudana.

Taron na yau Talata ya samu halartar manyan shugabannin da suka hada da firaminista Li Keqiang, Liu Yunshan da kuma mataimatin firaminista Zhang Gaoli. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China