in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta bukaci Japan da ta bayyana irin ta'asar da ta aikata a lokacin yaki
2015-08-07 21:00:54 cri
Kasar Sin ta bukaci Japan da ta bayyana karara irin laifuffukan yakin da ta aikata, a dai-dai lokacin da ake sa ran firaminista Shinzo Abe na Japan din ke shirin gabatar da jawabin bikin tunawa da shekaru 70 da kawo karshen yakin duniya na biyu a wannan mako.

Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Madam Hua Chunying ta shaidawa taron manema labarai a yau cewa, kasar Sin da ragowar kasashen da ke yankin Asiya da kuma duniya baki daya, suna jiran irin jawaban da shugabannin na Japan za su yi a game da wannan biki. Ta ce, kasar Sin tana bukatar Japan da ta amince da irin ta'asar da sojojin suka aikata.

Bayanai na nuna cewa, galibin kasashen da ke yankin Asiya na nuna damuwa cewa, Abe na iya gurbata gafarar da tsohon firaministan kasar Tomiichi Murayama ya yi a mukumance a shekarar 1995 a jawabin da zai yi. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China