in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wata kotu a Libya ta yanke wa Seif al-Islam Qaddafi hukuncin kisa
2015-07-28 20:58:15 cri

A Talatar nan ne wasu kafofin watsa labarai na kasar Libya, suka labarta cewa wata kotu dake zaman ta a birnin Tripoli, ta yankewa wasu tsoffin manyan jami'an gwamnatin Gaddafi sama da su 30 hukunci, ciki hadda dan tsohon shugaban kasar, Seif al-Islam Qaddafi,wanda aka yanke masa hukuncin kisa.

Ban da Seif al-Islam Qaddafi, wadanda aka yankewa hukuncin kisan sun hada da tsohon firaministan kasar Al-Baghdadi Ali Al-Mahmoudi, da tsohon shugaban hukumar leken asirin kasar Abdullah al-Sanoussi da sauransu.

Seif al-Islam Qaddafi dai bai bayyana a zaman kotun ba. Sai dai ya saurari hukuncin da kotun ta yanke masa ta yanar gizo. Ana dai tsare da Seif al-Islam a Zintan dake da tazarar kilomita 150 daga birnin Tripoli a kudu maso yammacin kasar, tun cikin shekarar 2011 ya zuwa wannan lokaci da aka yanke masa hukuncin kisa.

Sakamakon mamaye birnin Tripoli da kungiyar masu ra'ayin addini ta Fajr Libya ta yi a watan Agustan bara, tare da kafa gwamnatin ceton kasa, ya tilastawa gwamnatin wucin gadin Libiyan kaura zuwa gabashin kasar. A kuma wannan lokaci ta yi kira ga kasashen duniya da su yi watsi da wannan hukunci wanda ta ce an yanke shi ba bisa ka'ida ba.

A jiya Litinin ma'aikatar kula da harkokin shari'a ta gwamnatin wucin gadi a Libiyan ta fidda wata sanarwa wadda ke cewa hukuncin da wannan kotu za ta yanke ya sabawa doka. Kuma alkalin zai yanke hukuncin ne ala tilas karkashin matsin lamba. (Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China