in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin Sin a MDD: ya kamata a sanya kawar da talauci a matsayin muhimmin buri a ajendar samun bunkasuwa bayan shekarar 2015
2015-07-09 14:25:51 cri
Mataimakin zaunannen wakilin Sin dake MDD Wang Min, ya bayyana cewa kamata ya yi a ba da muhimmanci ga kudurin kawar da talauci a ajendar samun bunkasuwa bayan shekarar 2015.

Mr. Wang ya ce daukar wannan mataki na da nasaba da burin samun rayuwa da bunkasuwar jama'a mai inganci a kasashen duniya, idan aka yi la'akari da burin kasashe masu tasowa na raya tattalin arziki da zamantakewar al'ummar su.

Wang Min ya bayyana hakan ne a jawabin da ya gabatar, yayin muhawarar da ta gudana a taron koli, na majalisar kula da harkokin tattalin arziki da zamantakewar al'umma ta MDD na shekarar 2015 a jiya Laraba.

Ya ce kamata ya yi kasashen duniya su dora muhimmanci game da kudurin kawar da talauci, da sa kaimi ga samun bunkasuwa, hakan, a cewarsa zai taimaka a tinkari sabbin kalubalen dake shafar rashin ci gaban tattalin arziki cikin sauri, da tsaron makamashi, da sauyin yanayi da dai sauransu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China