in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tattalin arzikin Ghana na daf da farfadowa, in ji ministan kudin kasar
2015-05-21 10:15:37 cri

Ministan ma'aikatar kudin kasar Ghana Seth Terkper, ya yi hasashen farfadowar tattakin arzikin kasarsa nan da wani dan lokaci. Mr. Terkper ya bayyana hakan ne a jiya Laraba, yayin wani taron masana da kwararru a fannin tattalin arziki da ya gudana a birnin Accra.

A cewarsa, tattalin arzikin Ghana ya samu bunkasa zuwa matsayi na koli da kaso 15 bisa dari a shekarar 2011, kafin ya yi mummunar faduwa zuwa kaso 4.4 a bara. Sai dai duk da halin da ake ciki a yanzu haka, ministan ya ce, ana sa ran dagawar mizaninsa da kaso 8 cikin dari, sama da hasashen da aka yi a baya.

Sai da fa Mr. Terkper ya ce, dole a dauki wasu muhimman matakai, idan har ana da son cimma wannan buri, ciki hadda ririta kudade, da kare tattalin arzikin kasar daga almundahana. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China