in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yawan kudin dake kunshe cikin sabbin yarjejeniyoyin gine-gine da Sin ta daddale a nahiyar Afirka a farkon watanni 3 na bana sun karu da 49.4%
2015-05-15 15:55:53 cri
Ma'aikatar kasuwanci ta kasar Sin, ta ce yawan kudin dake kunshe cikin sabbin yarjejeniyoyin gine-gine da Sin ta daddale a nahiyar Afirka, cikin watanni 3 na farkon wannan shekara ya kai dala biliyan 23.11, adadin da ya karu da kashi 49.4 cikin dari bisa na makamancin lokaci a bara.

Kakakin ma'aikatar Shen Danyang ne ya bayyana hakan a Jumma'ar nan, yana mai cewa cikin kasashe 10 dake kan gaba a yawan yarjejeniyoyin da suka daddale tare da kasar ta Sin, 7 kasashe ne na nahiyar Afirka, kuma ana samun babban ci gaba a fannin zuba jari a manyan ayyuka a nahiyar.

Shen Danyang ya kara da cewa, yanzu haka ana fuskantar matsin lamba a bangaren raguwar bunkasar tattalin arzikin nahiyar Afirka, don haka kasar Sin ke fatan za a yi amfani da damar taron ministoci karo na 6, na dandalin tattaunawa kan hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Afirka da za a gudanar a bana, don gaggauta sa kaimi ga hadin gwiwar tattalin arziki, da cinikayya a tsakanin sassan, da kuma kyautata tsarin da ake da shi a wannan fanni. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China