in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babu wata kasa da ta nuna sha'awa kan shirin da Amurka da Philippines suka gabatar game da batun tekun kudancin kasar Sin
2014-08-12 11:04:34 cri
Yayin taron ministocin harkokin wajen kasashe mambobin kungiyar kudu maso gabashin Asiya ASEAN da ya gudana a kasar Myanmar a 'yan kwanankin baya, kasashen Amurka da Philippines sun sanar da manufar su, game da batun tekun kudancin kasar Sin, sai dai babu wata kasa ta nuna sha'awa game da manufofin na su.

A gun taron jami'an Sin da na sauran kasashen kungiyar ta ASEAN sun bayyana cewa, babu wata kasa da ke goyon bayan manufar dakatar da ayyuka a tekun kudancin kasar Sin wanda kasar Amurka ta gabatar.

Jami'an sun bayyana cewa, yayin taron ministocin harkokin wajen kasashe kungiyar ASEAN, wasu kasashe sun bayyana tabarbarewar dangantaka tsakanin Sin da wasu kasashe mambobin kungiyar ASEAN, duk kuwa da cewa wannan batu ne da ba shi da tushe bare makama. Hasali ma dai kasar Sin da kungiyar ASEAN, sun amince da batutuwan dake kunshe cikin sanarwar da aka fitar, wadda ta dace da ra'ayoyinsu da aka cimma a baya. Koda yake wasu kasashe sun sauya hakan da gangan, lamarin da ya nuna cewa, ba sa kan gaskiya game da wannan batu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China