in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta bukaci Amurka da ta kauracewa tsoma baki a sha'anin yankin Hong Kong
2015-04-14 20:08:05 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hong Lei, ya ce kasarsa na fatan Amurka za ta kauracewa tsoma baki cikin sha'anin yankin Hong Kong, duba da cewa wannan batu ne na cikin gidan kasar Sin, wanda kuma Amurkan ba ta da wani hurumi na sanya baki cikinsa.

Hong Lei ya bayyana hakan ne yayin taron manema labaru da ya gudana a Talatar nan, bayan da Amurkan ta fidda wani rahoto mai kunshe da yanayin da ake ciki, game da manufofin gudanarwar yankin na Hong Kong.

Bugu da kari, kakakin ma'aikatar wajen kasar ta Sin, ya yi kira ga Amurka da ta martaba alakar dake tsakaninta da Sin, ta hanyar daina sanya baki cikin al'amuran cikin gidan Sin, duba da cewa hakan ka iya lahanta kyakkyawar dangantakar dake tsakanin sassan biyu. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China