in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Harkokin Hongkong harkokin cikin gidan kasar Sin ne, in ji ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin
2014-12-04 20:17:11 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin malama Hun Chunying ta bayyana a yayin taron manema labaru da aka saba shiryawa a nan Beijing, yau cewa, harkokin yankin Hongkong harkokin cikin gidan kasar Sin ne. Bangaren kasar Sin na tsayawa tsayin daka kan matsayin kin amince da sauran kasashen duniya su tsoma baki cikin harkokin yankin Hongkong ta kowane irin salo.

Bisa labarin da aka bayar, an ce, a kwanan baya, madam Daniel Russel, mai ba da taimako ga sakataren harkokin wajen kasar Amurka ta ce, babu hannun kasashen waje a lamarin mamaye wasu tituna a yankin Hongkong, sannan ba hannun kasar Amurka a tashin hankalin. Sabo da haka, bangaren Amurka ya nemi bangaren Sin da ya yi hakuri, kuma ya bar al'ummar Hongkong su bayyana abubuwan da suke son fada. Game da wannan furucin da madam Daniel Russel ta yi, madam Hua Chunying ta bayyana matsayin da bangaren Sin ke dauka. Kuma ta jaddada cewa, tabbatar da kwanciyar hankali da bunkasuwa a Hongkong cikin dogon lokaci ba ma kawai yana dacewa da moriyar kasar Sin ba, har ma yana dacewa da moriyar bangarori daban daban baki daya. Sabo da haka, bangaren Sin yana fatan sauran kasashe za su rika yin abubuwa kamar yadda suka fadi, kuma su cika alkawuransu, su rika yin abubuwan da za su taimaka wajen tabbatar da kwanciyar hankali da bunkasuwa a Hongkong maimakon tayar da zaune tsaye. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China