in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Tunisia ta kama dukkan mutanen da ake zarginsu da hannu cikin harin da aka yi wa dakin ajiye kayayyakin tarihi na Bardo
2015-04-03 15:07:35 cri
Ma'aikatar harkokin cikin gida ta kasar Tunisia ta bayar da sanarwa a daren alhamis cewa, 'yan sandan kasar sun riga sun kama dukkan mutane 46 da aka zarge su da aikata laifin kai hari gaake zarginsu da hannu cikin harin da aka yi wa dakin ajiye kayayyakin tarihi na Bardo.

Sanarwar ta bayyana cewa, a wannan ranar 'yan sandan kasar sun kama mutane 21 da aka zarge su da aikata laifin kai harin, wadanda su ne membobin kungiyoyi biyu na dakaru a kasar. Ya zuwa yanzu, an riga an kama dukkan mutanen 46 dake da nasabaalakar kai tsaye da harin ta'addanci da aka kai ga dakin ajiye kayayyakin tarihi na Bardo kai tsaye.

A ranar 18 ga watan Maris, an kai hari ga dakin ajiye kayayyakin tarihi na Bardo a kasar Tunisia, wanda ya haddasa mutuwar mutane 23, yayin da mutane fiye da 40 suka ji rauni. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China