in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugabannin wasu kasashen duniya sun halarci zanga-zangar yaki da ta'addanci a kasar Tunisia
2015-03-30 15:23:03 cri

Don tunawa da mutanen da suka mutu a sakamakon harin da aka kai ga wurin ajiye kayayyakin tarihi na Bardo, da yin kira ga nuna goyon baya ga kasar Tunisia wajen yaki da ta'addanci, shugaban kasar Faransa François Hollande, shugaban Palesdinu Mahmoud Abbas da sauran shugabannin kasashen duniya sun halarci zanga-zangar yaki da ta'addanci da aka yi a babban birnin kasar Tunisia a ranar lahadi.

A safiyar wannan rana, a karkashin jagorancin shugaban kasar Tunisia Beji Caid Essibsi, jama'ar kasar fiye da dubu daya da shugabannin kasashen duniya da suka nuna goyon baya ga kasar sun yin zanga-zanga tun daga unguwar Bab Saadoun zuwa wurin ajiye kayayyakin tarihi na Bardo.

Bayan da masu zanga-zangar suka isa wurin ajiye kayayyakin tarihi na Bardo, shugaba Essibsi ya shugabanci bikin tunawa da mutanen da suka mutu a sakamakon harin da aka kai ga wurin Bardo, kana ya yaye gyalle a kan kabarin su. Essibsi ya bayyana cewa, an yi zanga-zangar ne don nuna cewa, jama'ar kasar Tunisia ba sa jin tsoron ta'addanci, kuma ba su kadai ba ne ke yaki da shi. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China