in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD na kokarin warware rikicin manoma da makiyayya a arewacin Cote d'Ivoire
2015-03-16 11:46:46 cri

Kwararrun tawagar MDD dake kasar Cote d'Ivoire (ONUCI) na dukufa wajen warware rikicin dake kamari tsakanin manoma da makiyayya a arewacin kasar, a wani labarin da Xinhua ya samu daga wata majiyar MDD a ranar Lahadi.

A cewar wani ofisan bangaren da ke kula da harkokin fararen hula na ONUCI mista Peyogori Ouattara, kwararru da hukumomin wuraren na yankunan dake arewacin kasar sun hada kokarinsu tare domin kai ga cimma wata hanyar sulhu tsakanin manoman da makiyayan.

Mista Ouattara ya yi amfani da misali na yankin Bako dake arewacin kasar, inda manoma da makiyayya suka cimma yarjejeniyar kawo karshen duk wani rikici da tashin hankali tsakaninsu. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China