in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mali ta sanar da kawo karshen cutar Ebola
2015-01-19 15:56:28 cri
A jiya ne gwamnatin kasar Mali ta sanar cewa, babu wani sabon rahoto na wani mutum da aka tabbatar ya kamu da cutar Ebola a cikin kwanaki 42 a jere, lamarin da ke shaida cewa an kawo karshen cutar Ebola a kasar.

Ofishin tawagar MDD mai kula da cutar Ebola dake kasar Mali ya bayar da sanarwa cewa, bisa ma'aunin hukumar kiwon lafiya ta duniya wato WHO, idan ba a gano sabbin mutanen da aka tabbatar sun kamu da cutar Ebola a cikin kwanaki 42 a jere ba, ana iya sanar da cewa,an kawo karshen cutar a kasar. Wannan na cewa, yanzu kasar Mali ta kawar da cutar Ebola a kasar.

Bisa kididdigar da hukumar WHO ta yi, an ce, tun lokacin da cutar Ebola ta bulla a shekarar bara, mutane 21296 suka kamu da cutar, yayin da kuma mutane 8429 suka mutu a sakamakon cutar. Yayin da yawan mutanen da suka mutu a sakamakon cutar a kasar Mali ya kai 7. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China