in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhun MDD ya kalubalanci bangarorin Mali da su cimma matsaya kan batun shimfida zaman lafiya
2015-02-07 17:22:49 cri
Kwamitin sulhun MDD ya fidda wata sanarwar dake kira ga bangaren gwamnatin Mali da na kungiyoyin 'yan adawar kasar, da su gaggauta farfado da shawarwari, ta yadda za su kai ga cimma matsayar dawo da yanayin zaman lafiya a dukkanin fannoni.

Kwamitin sulhun MDD ya nuna rashin jin dadi ga ci gaba da barkewar tashe-tashen hankula a arewacin kasar, lamarin dake haddasa rasa rayuka, tare da jikkatar fararen hula. Don gane da hakan ne kwamitin ya bukaci bangarori daban daban, dasu dakatar da ayyukan nuna karfin tuwa, tare da rungumar yarjejeniyar tsagaita bude wuta da suka daddale a bara.

Ban da wannan, kwamitin sulhu ya ce zai nazarci bukatar kakaba takunkumi ga wadanda ke da hannu cikin daukar matakan nuna karfi, da masu keta yarjejeniyar tsagaita bude wuta a Malin.

Kawo yanzu dai ana ci gaba da fama da tashe-tashen hankalu a arewacin Kasar ta Mali. Koda yake kasar Algeria, da MDD, da sauran masu ruwa da tsaki na ci gaba da shiga tsakani, inda ake fatan farfado da shawarwari tsakanin bangarorin kasar biyu a ranar 8 ga watan nan a birnin Algiers.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China