in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin kundumbala na kasar Sin sun tashi zuwa Sudan ta Kudu
2015-02-27 14:11:57 cri

Dakarun sojin kundumbala 144 na kasar Sin da za su yi aiki cikin tawagar wanzar da zaman lafiya ta MDD, sun tashi daga birnin Jinan zuwa kasar Sudan ta Kudu ta jirgin saman musamman na MDD.

Yayin bikin ban kwana da su karkashin jagorancin shugaban reshen sojojin kasa na kiyaye zaman lafiya Wang Zhen, sojojin sun rera taken kasa, sannan sun jaddada aniyyarsu game da cimma burin kiyaye zaman lafiya a karkashin tutar kasar Sin.

Ana sa rana da isar su Sudan ta Kudun, dakarun na Sin za su fara ayyukan binciken yanayin kasar, da kafa sansanin soja, da karbar na'urorin soja da kuma sauran ayyuka.

Rahotanni sun ce sauran sojoji da jami'ai 520 na reshen sojojin kasa masu aikin kiyaye zaman lafiya na kasar Sin, za su isa kasar ta Sudan ta Kudu a lokuta daban daban. (Lami)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China