in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-moon ya yi kira da a kara kwazo game da batun warware rikicin Sudan ta Kudu
2015-02-04 10:30:13 cri

Babban magatakardar MDD Ban Ki-moon, ya sake jaddada kira ga daukacin masu ruwa da tsaki, da su zage-damtse wajen tabbatar da nasarar shirin wanzar da zaman lafiya a Sudan ta Kudu.

Hakan dai na zuwa ne bayan da bangarorin kasar biyu suka amince da wata sabuwar yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin su.

Cikin wata sanarwa da kakakinsa ya fitar, Mr. Ban ya jaddada cewa, babu wata nasara da za a cimma a Sudan ta Kudun, muddin shuwagabannin bangarorin kasar biyu suka ki amincewa, su sanya bukatun al'ummun kasar gaban nasu muradun.

Mr. Ban ya kuma bukace su, da su shirya tinkarar zagaye na biyu na ganawar da za su gudanar, da niyar gaggauta kawo karshen rikicin kasar baki daya.

Kaza lika babban magatakardar MDDr ya jinjinawa kungiyar shuwagabannin kasashen gabashin Afirka ta IGAD, bisa shiga tsakani da ta yi a rikicin kasar ta Sudan ta Kudu.

Kungiyar ta IGAD ce dai ta jagoranci shirin shiga tsakani, wanda ya kai ga cimma matsaya guda tsakanin shugaban Sudan ta Kudu Salva Kiir, da shugaban 'yan adawa, kuma tsohon mataimakin shugaban kasar Riek Machar, yayin zaman sulhun da ya gudana a ranar Litinin, a birnin Addis Ababan kasar Habasha. Yarjejeniyar da aka cimma ta kuma tanaji sake tattaunawa, a wani mataki na kammala shirin wanzar da zaman lafiya, daga nan zuwa 5 ga watan Maris mai zuwa. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China