in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a jinkirtar da babban zaben shugaban kasar Nijeriya
2015-02-08 16:57:29 cri
Jiya Asabar 7 ga wata da dare, shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasar Nijeriya Attahiru Jega ya sanar a babban birnin kasar, Abuja cewa, za a jinkirtar da babban zaben shugaban kasar zuwa ranar 28 ga watan Maris, kuma za a gabatar da sunayen gwamnoni da 'yan majalisar dokoki na jihohin kasar a ran 11 ga watan Afrilu.

Mista Jega ya yi wannan furuci a yayin wani taron manema labarai, bayan tattaunawarsa da wasu manyan jami'an da abin ya shafa ta tsawon lokaci kan batun zabukan Najeriya. Ya ce, sabo da ci gaban hare-haren da Boko Haram suke kai a yankunan gabas maso arewacin kasar, sojojin kasar ba su iya tabbatar da tsaron kasar a yayin babban zaben ba, dalilin hakan, an yanke shawara cewa ya kamata a jinkirtar da lokacin babban zaben shugaban kasar, da kuma zaben gwamnonin jihohi da na 'yan majalisar dokokin kasar. Mista Jega na fatan za a iya tabbatar da tsaro a dukkan fadin kasar Nijeriya a yayin babban zabe.

Bisa ga abin da aka tsara a baya, an ce za'a gudanar da zaben shugaban kasar a ran 14 ga watan nan da muke ciki, a yayin da zaben gwamnoni jihohi da na 'yan majalisar dokoki a ran 28 ga watan, amma aka jinkirtar da lokacin zabukan bisa dalilan tsaro. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China